Annobar cutar kwalara ta kashe mutane 7 a Jigawa

An samu ɓarkewar annobar cutar kwalara a ƙaramar hukumar Kirikasamma da kewayenta a jihar Jigawa.

Kawo yanzu mutane 7 aka tabbatar da mutuwarsu sanadiyar annobar a yayin a wasu da dama ke can kwance a asibiti inda suke karbar magani.

Jami’in tsare-tsare na hukumar kula da lafiya a matakin farko na Æ™aramar hukumar Kirikasamma, Musa Abdullahi Digadige ya ce É“arkewar annobar cutar ta shafi Æ™auyuka da dama da suka haÉ—a da Malori, Maikintari, Dilmari, Kirikasamma, da kuma wani sashe na na Æ™auyen Baturiya.

A cewar Digadige alamomin cutar sun haɗa da gudawa,  ƙullewar ciki, jin yin amai, amai da kuma zazzaɓi.

Shugaban Sashen Ruwa da Tsafta, Muhammad Maisamari ya ce an tura tawagar jami’an kiwon lafiya ya zuwa yankunan da abun ya shafa domin su bayar da kulawar  da ta kamata.

Ƙaramar hukumar ta kuma sayo magunguna da sauran kayayyakin da suka kamata domin samun nasarar maganin cutar.

Daraktan mulki da gudanarwa na ƙaramar hukumar, Idris Gambo Abubakar ya yi alƙawarin bayar da dukkanin taimakon da ya dace domin daƙile yaɗuwar cutar.

Hukumomi sun alaƙanta ɓarkewar cutar da gurɓatar ruwan sha sanadiyar ambaliyar ruwa da aka samu a yankin sanadiyyar mamakon ruwan sama.

More News

Atiku ya bayar da tallafin miliyan 100 ga mutanen da ambaliyar ruwa ta shafa a Maiduguri

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar ya bayar da gudunmawar naira miliyan 100 ga mutanen da ambaliyar ruwa ta shafa a Maiduguri babban birnin...

An saki Sowore bayan kama shi da aka yi  a filin jirgin saman Lagos

Omoyele Sowore ɗantakarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam'iyar AAC a zaɓen 2023 a ranar Litinin ya ce an tsare shi na gajeren lokaci a...

An saki Sowore bayan kama shi da aka yi  a filin jirgin saman Lagos

Omoyele Sowore ɗantakarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam'iyar AAC a zaɓen 2023 a ranar Litinin ya ce an tsare shi na gajeren lokaci a...

Mutanen Sokoto na ta murnar kashe ƙasurgumin ɗanbindigar nan Halilu Buzu

Mazauna yankin Sokoto da kewaye na murnar kashe wani kasurgumin shugaban ‘yan bindiga, Kachallah Halilu Buzu, da sojojin Najeriya suka yi a farmakin da...