Kwamishinan ‘yan sanda na jihar Delta, Wale Abass ya bayar da umarnin janye karar lalata da wani dalibi dan shekara hudu da wani mutum mai shekaru 46 ya yi daga kotu domin gudanar da bincike mai kyau.
Da yake magana a madadin Kwamishinan ƴan sanda, mai magana da yawun rundunar, DSP Bright Edafe, ya bayyana hakan yayin da yake gabatar da wanda ake zargin a ranar Asabar a Asaba.
Ya ce, “Rundunar ta na sane da wani labari da aka buga a kafafen sada zumunta daban-daban kan zargin lalata da wani Innocent Ezeukwu, mai shekaru 46, mai kula da makarantar Great Leader International School ya yi da yarinya ƴar shekara huɗu.
“A ranar 5 ga Oktoba, 2023, wata Misis Joy Chukwudi ta ruwaito cewa yayin da take wankan ‘yarta ‘yar shekara hudu, ta gano wani tabon jini a gaban ‘yarta.”
“Kwamandan yankin Agbor ya yi karin bayani kan tawagar masu binciken da za su ci gaba da zuwa wurin wanda ake zargi da aikata laifin kuma an kama wanda ake zargin Innocent Ezeukwu.