Ana Gardama Kan Cancantar Gina Jami’ar Sufuri a Daura

Kwararru a fannin ilimi sun nuna cewa gina irin wanan Jami’ar da za ta koya wa matasa yadda za su sarrafa ababen hawa musamman ma jiragen kasa, da yanzu ake amfani da shi, abu ne mai alfanu a kasa kuma zai ba matasa damar dogaro da kansu duk da cewa ana cikin wani yanayi na raguwar tattalin arziki. Farfesa Sani Sambo na Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zaria yana cikin masu wanan tunanin inda ya ce a duk lokacinda aka ce Jami’a za a yi to abu ne da ya kamata yan kasa su yi na’am da ita ba wai a yi ta suka akai ba domin matasa da ke fama da rashin aikin yi za su amfana kuma a haka kasa ce za ta amfana.

To sai dai ga daya daga cikin Dattawan Arewa Dr. Usman Bugaje gina Jami’ar a Daura bai dace ba, domin a kwanan nan aka kafa wata Makarantan Kimiya da fasaha a Daura, saboda haka wanan abu bambadanci ne kawai mutane ke yi, kuma shugaban Kasa ake so a burge kuma yin haka rashin adalci ne. Bugaje ya ce sannu a hankali ma za a ce sai shugaban Kasa ne zai za6i shuwagabanin Jami’ar kuma haka zai kawo rashin jituwa.

Amma wani kwararre a fannin ilimi na bai daya, Hassan Sardauna Hammayo yana ganin yin wanan Jami’a a yanzu ya dace domin babu irin ta a kasa baki daya, kuma za a samu kwararru daga jami’ar wadanda za su habbaka fannin sufuri.

Shi kuwa mai nazari kan al’amuran yau da kullum, Abubakar Aliyu Umar ya ce ba kyauta ba ne, wannan ai cin fuska aka yi wa ‘yan kasa domin za a sa mutane cikin yanayin bauta ne kawai ga kasar China. Aliyu ya ce inda Shugaba Buharin da ya sani ada ne, da ya ce kar a kai Jami’ar Daura, saboda kar a ga kamar yana da hannu a ciki.

Abubakar Aliyu ya ce an yi rashin adalci saboda jami’o’in da ake da su yanzu suna neman rugujewa saboda rashin kula. Ya ce me zai hana a habba Cibiyar Koyar da dabarun sufuri da ke Zaria idan har ana so a samu cigaba mai dorewa?

Wanan Jami’a da Kamfanin CCECC ta Kasar China ke ginawa a kyauta za ta lakume kudi har dalar Amurka miliyan 50.

More News

Zanga-zanga: An jibge Æ´an sanda 4200 a Abuja

Rundunar Æ´an sandan birnin tarayya Abuja ta tura Æ´an sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haÆ™uri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...