Ana ci gaba da zanga-zanga a rana ta uku a Legabon

Masu zanga-zangar a kusa da ginin majalisar kasar rika sun jefawa 'yan sanda wuta, da duwatsu

Bayanan hoto,
Masu zanga-zangar a kusa da ginin majalisar kasar rika sun jefawa ‘yan sanda wuta, da duwatsu

A rana ta uku a jere, a na cigaba da arangama tsakanin jami’an tsaro da masu zanga-zanga a Beirut babban birnin Lebanon, yayin da jama’a ke nuna fushinsu a kan fashewar nan da ta janyo rasa rayukan fiye da mutane 200.

Zanga-zangar ta ci gaba duk da murabus din da gwamnati ta yi a ranar Litinin, inda mutane da yawa ke zargin ministocin da sakaci.

Masu zanga-zanga a kusa da ginin majalisar kasar rika sun jefawa ‘yan sanda wuta, da duwatsu da abubuwan fashewa, yayin da ‘yan sandan ke maida martani da gurneti da kuma barkonon tsohuwa.

Da yake sanar da murabus dinsa Firai ministan kasar, Hassan Diab, ya nisanta kansa da alhakin fashewar, ya kuma ce shirye-shiryensa na kawo sauyi ne ga tsarin siyasar kasar da aka gurbata.

Ko da a kwanan baya, kasar ta yi fama da mummunan rikicin tattalin arzikin kasar.

Bayanan hoto,
Fira ministan kasar, Hassan Diab,

Mene ne sanadin fashewar ?

Shugaban Lebanon Michel Aoun ya É—ora alhakin fashewar tan 2,750 na sinadarin ammonium nitrate da aka jibge cikin wani É—akin ajiyar kaya na tashar jirgin ruwan birnin.

A shekarar 2013, wani jirgin ruwa mai suna MV Rhosus yayi jigilar sinadarin. Bayan ya yada zango a tashar jirgin ruwa na Beirut saboda wata matsalar inji a kan hanyarsa daga ƙasar Georgia zuwa Mozambique, sai hukumomin tashar suka hana shi barin tashar bayan sun binciki kayan da yake ɗauke da su.

Kamar yadda shafin intanet na Shiparrested.com ya ruwaito, masu jirgin ruwan sun yi watsi da lamarin jirgin ruwan nasu a tashar, lamarin da yasa aka kwashe sinadarin daga ciki zuwa wani É—akin ajiya mai lamba 12 bayan wata kotu ta bayar da umarnin yin haka.

Tun wancan lokacin sinadarin ke jibge cikin É—akin, maimakon a sayar da shi ko dai a raba shi da wurin.

Shugaba Aoun ya yi alƙawarin gudanar da cikakken bincike kan fashewar.

“Mun Ć™uduri niyyar ci gaba da bincike kuma za mu bayyana yadda wannan abin takaicin ya auku ba tare da jinkiri ba, kuma duk wadanda aka samu da sakaci da ya janyo fashewar za su É—andana kuÉ—arsu,” inji shugaban ranar Laraba bayan ya zaga cikin tashar jirgin ruwan.

Firai minista Hassan Diab ya bayyana yadda aka bari fasewar ta auku “abin da ba za a amince da shi ba.”

More News

Yadda rikici a kan gishirin N20 ya yi sanadiyyar mutuwar wani mutum a Kano

Wani magidanci mai suna Zakari Hamza mai shekaru 45, ya gamu da ajalinsa a hannun kanen matarsa, wani Magaji Salisu saboda gishirin N20. Dan marigayin,...

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan IPOB 5

Dakarun rundunar sojan Najeriya da kuma ta rundunar sojan ruwan Najeriya a ranar Talata sun kashe mayaƙan ƙungiyar IPOB guda biyar a yayin musayar...

ĆŠan agajin Izala ya samu lambar yabo, kujerar hajji, kyautar mota bayan ya tsinci naira miliyan 100 ya mayar wa mai su

Salihu AbdulHadi Kankia, mamba ne na kungiyar agaji ta kungiyar Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa Iqamatus Sunnah (JIBWIS), ya samu yabo da tukuicin mayar da...

Musulmi a Zaria sun yi taron addu’o’i saboda mummunan halin matsi da Najeriya ke ciki

Musulmi a garin Zaria na jihar Kaduna, sun gudanar da addu'a ta musamman domin neman taimakon Allah kan halin da 'yan Najeriya ke ciki...