Kwale-kwale ya kifa inda ake kyautata zaton cewa mutanen ciki sun nitse a ruwa a lokacin da suka sami hatsari a Yauri da ke jihar Kebbi.
Lamarin ya faru ne a ranar Litinin, inda ake danganta hatsarin sakamakon rashin kyawun yanayi da mamakon ruwan sama a kogin Niger da ya ratsa jihar Kebbi.
Wani ganau, Haruna Rafin Kuka Yauri, ya ce ana can ana ci gaba da duba gawawwakin mutanen da suka rasu.
Ya ce ba su kai ga gano adadin mutanen da suke cikin jirgin ba.
Shugaban karamar hukumar ta Yauri, Bala Muhammad Gagga, ya ce an zakulo gawawwaki huÉ—u zuwa yanzu.