An yi ƙone-ƙone a garin Lafiya kan hukuncin kotun ƙoli da ya tabbatar da zaɓen Abdullahi Sule

Wasu rukunin matasa sun fantsama kan tituna a ranar Juma’a inda suka gudanar da zanga-zangar nuna adawa da hukuncin kotun ƙoli da ya tabbatar da zaɓen, Abdullahi Sule a matsayin gwamnan jihar Nasarawa.

Gidan Talabijin na Channels ya rawaito cewa masu zanga-zangar sun ƙona tayoyi a gaban ginin ofishin jam’iyar PDP dake Lafiya.

Har ila yau masu zanga-zangar sun ƙona tayoyi akan babbar hanyar tafiya birnin Jos babban birnin jihar Filato.

Zanga-zangar ta jawo an rufe makarantu dama wuraren sana’a a birnin na Lafiya.

Tushen Abin Da Ya Faru

Biyo bayan ƙarar da ɗan takarar jam’iyar PDP a zaɓen gwamnan jihar, David Ombugadu ya shigar kotun sauraren kararrakin zaɓe ta tabbatar da shi a matsayin zaɓaɓɓen gwamnan jihar.

Gwamna Sule ya ɗaukaka ƙarar hukuncin inda kotun ɗaukaka ƙara ta tabbatar masa da nasarar da ya samu a zaɓen gwamnan jihar da aka yi.

Rashin gamsuwa da hukuncin kotun ɗaukaka karar ne ya sa Ombugadu ya ɗaukaka ƙara ya zuwa kotun ƙoli inda kuma a yau ta yanke hukuncin da ya bawa gwamna Sule nasara.

More from this stream

Recomended