An tsinci gawar yarinya ‘yar shekara 16 da aka jefa rijiya a Jigawa

An jefar da gawar wata yarinya ‘yar shekara 16 a cikin rijiya da ke karamar hukumar Ringim ta jihar Jigawa.

Wani dan uwan mamaciyar da ya sakaye sunansa, ya ce lamarin ya faru ne a kauyen Beguwa a ranar Asabar din da ta gabata.

Ya ce an fara bayyana cewa marigayiyar ta bace kafin a gano gawarta a ranar Laraba, kwanaki hudu bayan faruwar lamarin, yayin da wasu manoma da ke kan hanyarsu ta zuwa gona suka ji wani wari.

Ya ce tare da taimakon hukumar kashe gobara, jami’an tsaro, da samari nagari, an dauki gawar tare da binne ta bisa ga shari’ar Musulunci.

Ya yi zargin cewa saurayinta da abokansa ne suka yi wa marigayiyar fyade, inda suka jefar da gawarta a cikin wata rijiya da ke wajen kauyen.

More News

Lauya ya nemi kotu ta bashi mako 4 ya nemo inda Yahaya Bello ya ɓuya

Abdulwahab Mohammed babban lauyan tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya nemi babbar kotun tarayya dake Abuja da ta bashi makonni huɗu domin ya...

Ɗalibai 9 aka tabbatar da yin garkuwa da su daga jami’an jihar Kogi

Gwamnatin jihar Kogi ta tabbatar da cewa ɗalibai 9 aka tabbatar sun ɓace bayan da wasu ƴan bindiga suka kai farmaki Jami'ar Kimiya da...

Mayaƙan Boko Haram Biyu Sun Miƙa Kansu Ga Sojoji

Aƙalla mayaƙan Boko Haram biyu ne suka miƙa kansu ga dakarun sojan Najeriya na rundunar Operation Haɗin Kai a yankin gabashin jihar Borno. Mayaƙan biyu...

Isa Dogonyaro Ɗan Majalisar Tarayya Daga Jihar Jigawa Ya Rasu

Isa Dogonyaro wakilin al'ummar ƙananan hukumomin Garki da Baɓura a majalisar wakilai ta tarayya ya rasu. Ɗaya daga cikin abokan aikin marigayin a majalisar tarayya,...