An tsinci gawar yarinya ‘yar shekara 16 da aka jefa rijiya a Jigawa

An jefar da gawar wata yarinya ‘yar shekara 16 a cikin rijiya da ke karamar hukumar Ringim ta jihar Jigawa.

Wani dan uwan mamaciyar da ya sakaye sunansa, ya ce lamarin ya faru ne a kauyen Beguwa a ranar Asabar din da ta gabata.

Ya ce an fara bayyana cewa marigayiyar ta bace kafin a gano gawarta a ranar Laraba, kwanaki hudu bayan faruwar lamarin, yayin da wasu manoma da ke kan hanyarsu ta zuwa gona suka ji wani wari.

Ya ce tare da taimakon hukumar kashe gobara, jami’an tsaro, da samari nagari, an dauki gawar tare da binne ta bisa ga shari’ar Musulunci.

Ya yi zargin cewa saurayinta da abokansa ne suka yi wa marigayiyar fyade, inda suka jefar da gawarta a cikin wata rijiya da ke wajen kauyen.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]