An tabbatar da mutuwar mutane 6 a hatsarin jirgin kasa a Lagos

Mutane 6 aka tabbatar da mutuwar su a hatsarin jirgin kasar da ya rutsa da wata babbar motar fasinja a jihar Lagos.

Hatsarin ya faru ne da safiyar ranar Alhamis wajen unguwar Shogunle da Ikeja lokacin da motar ta nemi tsallaka layin dogon inda ta ci karo da jirgin dake tawowa.

Fasinjoji da dama ne suka jikkata a hatsarin inda aka kai su Asibitin Koyarwa na Jami’ar Jihar Lagos.

Da yake magana da yan jaridu a asibitin koyarwar, gwamnan jihar Babajide Sanwoolu ya ce an tabbatar da mutuwar huÉ—u daga cikin mutanen a asibitin.

Tun da farko an bada rahoton cewa biyu daga cikin mutanen da abin shafa sun mutu nan take a wurin da hatsarin ya faru.

Gwamnan ya kuma nemi jama’a da su bayar da tallafin jini a marasa lafiya.

More News

Zanga-zanga: An jibge Æ´an sanda 4200 a Abuja

Rundunar Æ´an sandan birnin tarayya Abuja ta tura Æ´an sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haÆ™uri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...