An tabbatar da mutuwar mutane 6 a hatsarin jirgin kasa a Lagos

Mutane 6 aka tabbatar da mutuwar su a hatsarin jirgin kasar da ya rutsa da wata babbar motar fasinja a jihar Lagos.

Hatsarin ya faru ne da safiyar ranar Alhamis wajen unguwar Shogunle da Ikeja lokacin da motar ta nemi tsallaka layin dogon inda ta ci karo da jirgin dake tawowa.

Fasinjoji da dama ne suka jikkata a hatsarin inda aka kai su Asibitin Koyarwa na Jami’ar Jihar Lagos.

Da yake magana da yan jaridu a asibitin koyarwar, gwamnan jihar Babajide Sanwoolu ya ce an tabbatar da mutuwar huÉ—u daga cikin mutanen a asibitin.

Tun da farko an bada rahoton cewa biyu daga cikin mutanen da abin shafa sun mutu nan take a wurin da hatsarin ya faru.

Gwamnan ya kuma nemi jama’a da su bayar da tallafin jini a marasa lafiya.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...