An Soke Zaben Fidda Gwani Na Jam’iyyar APC A Jihar Legas

Bayan da masu zabe suka shafe lokuta da dama suna zaben fidda gwani na gwamna a tutar APC a jihar Lagos, ‘yan kwamitin lura da zaben sunki amincewa da zaben tare da soke shi,kuma basu fadi ranar sake wani zaben ba, abinda magoya bayan wani dan takara ke zargin akwai lauje cikin nadi.

Shugaban kwamitin fidda gwanin takarar gwamna a jihar legas Mr. Clement Ebere ya bayyana soke zaben fidda gwanin dan takarar gwamna a jihar Legas inda yace kwamitin a shirye take da ta gudanar da zabe mai tsafta wanda zai samu amincewar kowane bangare daga cikun ‘yan takarar na jamiyyar APC.

Ya sjhaidawa yan jaridu cewa sun soke zaben ne domin kuwa har zuwa yammacin Talata basu samu cikakkun sunayen wakilan daya daga cikin ‘yan takarar da doka ta bada umarnin ace suna da shi ba, sai dai bai bayyana wanne daga cikin ‘yan takarar bane.

Zaben dai anayi tsakanin Babajide Olu ne dake samun goyon bayan shugaban jamiyyar ta APC Asiwaju Bola Tinubu da kuma gwamnan jihar Akinwome Ambode.

More News

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...

Mutane 18 sun ƙone ƙurmus a wani hatsarin mota

Aƙalla fasinjoji 18 ne suka ƙone ƙurmus a wani hatsarin mota da ya faru akan babbar hanyar Ojebu-Ode zuwa Ore a yankin Ogbere dake...

AMBALIYA: Bafarawa ya ba wa al’ummar Sokoto gudunmawar naira biliyan 1

Tsohon gwamnan jihar Sokoto, Alhaji Attahiru Bafarawa, ya bayar da gudummawar Naira biliyan daya ga al’ummar Sokoto, domin rage radadin wannan annoba.An bayyana hakan...

Ƴanbindiga sun kai hari coci-coci a Kaduna, sun kuma yi garkuwa da mutane

Mutane 3 ne ake fargabar sun mutu, sannan an yi garkuwa da wasu 30 bayan wani hari da wasu ‘yan bindiga suka kai a...