An sako karin mutane uku daga cikin fasinjojin jirgin kasar Abuja-Kaduna

Yan bindiga sun sako karin mutane uku daga cikin wadanda suka yi garkuwa da su a jirgin kasar da ya ta shi daga Abuja zuwa Kaduna .

A cikin wata ganawa da yayi da gidan rediyon BBC Hausa daya daga cikin mutanen da aka sako ya ce bashi da masaniyar biyan kudin fansa kafin a sako su.

Ya bayyana cewa sun sha bakar ukuba a hannun yan bindiga a kwanakin da suka shafe a hannunsu.

Sakin nasu na zuwa ne sama da wata hudu bayan da yan bindigar suka sace su akan hanyar su ta komawa daga Abuja zuwa Kaduna.

More News

Gobara ta kama wani sashe na kotun ƙolin Najeriya

An samu tashin gobara a wani sashe na Kotun Kolin Najeriya dake birnin tarayya Abuja. Kawo yanzu babu wani bayani kan musabbabin tashin gobarar amma...

Gobara ta kama wani sashe na kotun ƙolin Najeriya

An samu tashin gobara a wani sashe na Kotun Kolin Najeriya dake birnin tarayya Abuja. Kawo yanzu babu wani bayani kan musabbabin tashin gobarar amma...

Yan bindiga sun sace kwamishinan yaÉ—a labarai na Benue

Yan bindiga sun yi garkuwa da, Matthew Abo Kwamishinan Yada Labarai, Al'adu da Yawon Bude Ido na jihar Benue. An yi garkuwa da Abo a...

Nan bada jimawa za a kawo karshen rashin wutar lantarki a Kebbi

Gwamnatin jihar Kebbi ta roki mazauna jihar da su kara hakuri inda ta ce rashin wutar lantarki da ake fuskanta a jihar zai zo...