An Sake Yin Zanga-Zanga A Jihar Niger Kan Tsadar Rayuwa

Wasu mazauna garin Suleja dake jihar Niger sun fantsama kan tituna domin yin zanga-zanga kan tsadar rayuwa da ake fama da ita a kasarnan.

Da yake magan da jaridar The Cable ranar Laraba, Sadiq Suleja dan takarar majalisar jiha karkashin jam’iyar PRP a mazabar Suleja ya ce masu zanga-zangar sun taru inda suka fara ta da karfe 9 na safe.

Masu zanga-zangar na dauke da kwalaye da aka rubuta cewa “Yan Najeriya Na Shan Wahala A Kawo Karshen Wahalar Yanzu”.

A cewar Sadiq zanga-zangar da aka gudanar takaitacciya ce kuma bata samu halartar mutane masu yawa ba.

Wannan karo na biyu da ake makamanciyar irin wannan zanga-zangar a jihar Niger biyo bayan wacce aka yi a ranar Litinin.

More News

An kama wasu mutane biyu da hodar ibilis a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta sanar da kama wasu mutane biyu da aka samu ɗauke da ƙunshin hodar ibilis mai yawan gaske. Mai magana...

Ƴan sanda sun kama wani mutum ɗauke da bindigogi 20 a Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce jami'anta sun kama wani  riÆ™aƙƙen mai safarar bindiga inda aka same shi da bindigogin AK-47 Æ™irar gida...

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waÉ—anda suka...