An sake samun wani sabon tsagin shugabanci a jam’iyar ADC

Rikicin jam’iyar ADC na cigaba da kara tsamari bayan da wani tsagi ya sake bulla da ya ce bai yadda da shugabancin ɓangaren David Mark ba da kuma na Nafiu Bala.

Ƙungiyar shugabannin jihohi na jam’iyar ta ADC sun sanar da yin fatali da shugabancin Nafiu Bala da kuma na David Mark

Da yake magana a yayin wani taron manema labarai a Abuja, Don Obinna  shugaban jam’iyar na jihar Abia ya ce Mark da Bala sun kwace ikon jam’iyar daga halastattun ƴaƴanta.

Ya goyi bayan matakin da hukumar zabe ta INEC ta dauka na janye amincewa da shugabancin David Mark.

Obinna ya ce har yanzu Dumebi Kachikwu mutumin da ya yiwa jam’iyyar takarar shugaban kasa a zaɓen 2023 halastaccen dan jam’iyar ne saboda korar da aka yi masa ta saba ka’ida.

More from this stream

Recomended