A ranar Laraba ne gwamnatin jihar Kano ta kafa dokar hana fita ta sa’o’i 24 a jihar domin kaucewa tabarbarewar doka da oda biyo bayan korar Gwamna Abba Kabir Yusuf na jam’iyyar New Nigerian People’s Party da kotun sauraren kararrakin zaben gwamnan jihar ta yi.
An tsaurara matakan tsaro a duk fadin birnin Kano a ranar Laraba jim kadan bayan hukuncin da kotun sauraren kararrakin zabe ta mutum uku karkashin jagorancin Mai shari’a Oluyemi Akintan-Osadebay ta ayyana dan takarar jam’iyyar All Progressives Congress, Nasir Gawuna a matsayin wanda ya lashe zaben gwamna da aka gudanar a watan Maris 2023. a
Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Mohammed Gumel, wanda ya tabbatar da dokar hana fita a cikin wata sanarwa, ya ce dokar ta fara aiki ne daga karfe 6 na yammacin Laraba zuwa karfe 6 na yammacin ranar Alhamis (yau). Gumel ya sha alwashin tabbatar da bin umarnin da aka ba su, inda ya yi gargadin cewa za a kama wadanda suka saba wa doka kuma su fuskanci fushin doka.