An sace kusan mutane 19 a sabon harin da aka kai Katsina

Mazauna kauyukan karamar hukumar Batsari a jihar Katsina sun koka game da ci gaba da kai hare-haren ta’addanci.

A ranar Lahadin da ta gabata ne wasu ‘yan bindiga suka sace mutane 19 yawancinsu mata daga kauyen Madogara.

A cikin wannan samamen da aka kai cikin dare, an kama mata 16 da maza uku, tare da yara, wasu ‘yan kasa da shekara daya.

Wani jami’in lafiya daga garin Batsari da ya bukaci a sakaya sunansa saboda matsalolin tsaro, ya bayyana cewa a hankali Madogara ta koma baya.

Ya ce a kowane dare, mazauna kauyen na taruwa a gidajen tsakiyar kauyen don neman tsira kafin su koma gidajensu da safe.

More News

EFCC ta kama wasu masu hada-hadar canjin kuÉ—aÉ—e

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta kama wasu mutane 34 da take zargi suna da hannu wajen yiwa...

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...