An kwantar da shugaban NLC a asibiti bayan ya samu rauni a idonsa

Daga Sabiu Abdullahi

A halin yanzu dai ƙwararrun likitoci a asibitin koyarwa na jami’ar tarayya dake Owerri na kokarin ceto idanun Joe Ajaero, shugaban kungiyar kwadago ta Najeriya NLC, biyo bayan wani hari da aka yi musu a yayin wata zanga-zanga a jihar Imo ranar Laraba.

Rahotanni sun ce rundunar ‘yan sandan jihar Imo ta kama Ajaero a lokacin da yake jagorantar wata zanga-zanga, amma rundunar ta bayyana cewa an kubutar da shi daga hannun wasu gungun mutane ne.

Wani faifan bidiyo ya nuna yadda aka garzaya da Ajaero cibiyar kula da lafiya ta tarayya da ke Owerri a zaune a tsakanin wasu mutane biyu.

A cikin bidiyon, ya bayyana cewa ba shi da waya tare da shi amma yana fatar samun taimako daga wani dan uwan da ke aiki a FUTHO.

Jami’an NLC sun yi Allah wadai da lamarin, inda suka bayyana shi a matsayin wani yunkuri na sace mutane wanda ya rikide zuwa yunkurin kisan kai.

More News

Ƴansanda sun hallaka masu garkuwa da mutane

Ƴansanda sun hallaka wasu masu garkuwa da mutane uku da ake zargin sun yi yunkurin yin garkuwa da matar wani dan majalisar dokokin jihar...

Ƴansanda a Katsina sun yi nasarar cafke wasu tantiran masu safarar alburusai wa ƴanbindiga

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina a ranar Juma’a ta sanar da cewa ta kama wasu manyan ‘yan bindiga guda uku tare da kwato manyan...

Tinubu ya amince da mafi karancin albashi na N70,000

Shugaba Bola Tinubu ya amince da N70,000 a matsayin mafi karancin albashi ga ma’aikatan Najeriya, inda ya yi alkawarin sake duba dokar mafi karancin...

Mutanen Isra’ila sama da rabin miliyan sun tsere saboda yakin Gaza

Mutanen Isra'ila sama da rabin miliyan ɗaya ne suka fice daga ƙasar kuma ba su koma ba a watanni shida na farkon yaƙin Isra'ila...