An kashe mutum 59 a Borno

Kungiyar Boko Haram

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Wani hari da mayaka masu da’awar kishin addinin Islama suka kai jihar Borno ya halaka mutum kimanin 59.

Wadanda lamarin ya faru kan idanunsu sun ce mayakan ‘yan kungiyar ISWAP – wani tsagi na Boko Haram sun kutsa kauyen Gubio inda suka budewa jama’a wuta tare da bi ta kan wasu al’ummar garin.

Rahotanni sun ce ‘yan bindigar sun yi awon gaba da shanu da kuma rakuma.

Yankin na Gubio ya sha fuskantar irin wadannan hare-hare lamarin da ya sa al’ummar yankin suka yi shirin ko ta kwana domin kare kansu.

An shafe fiye da shekaru 10 hukumomi a Najeriya suna yaki da kungiyar Boko Haram – wacce ta yi sanadiyyar mutuwar dubban mutane tare da lalata dukiya ta miliyoyin naira.

Rikicin na Boko Haram wanda aka soma a jihar Borno da ke arewa maso gabashin Najeriya ya fantsama zuwa bakwabtan kasashe kamar su Nijar, Chadi da kuma Kamaru.

Gwamnatin Buhari dai ta dade tana ikirarin karya lagon kungiyar Boko Haram da ta addabi yankin arewa maso gabas, amma kuma har yanzu mayakan kungiyar na ci gaba da yi wa mutanen yankin barazana.

More News

Ƴan bindiga sun Æ™one ginin hedkwatar Æ™aramar hukuma tare da kashe jami’an tsaro

Ƴan bindiga sun kai farmaki hedkwatar ƙaramar hukumar, Isiala Mbano dake jihar Imo da tsakar daren ranar 3 ga watan Satumba inda suka ƙone...

An kama wasu Æ´anta’adda da ke da alaÆ™a da Turji

Akalla mayaka 18 da ke da alaka da fitaccen shugaban ‘yan ta’adda Bello Turji aka kama a jihar Sokoto da ke arewa maso yammacin...

Dakarun Najeriya sun kai farmaki wa Æ´an’adda a Borno, wani kwamanda ya miÆ™a wuya

Rundunar sojin Najeriya ta sanar a ranar Lahadin cewa dakarunta sun yi nasarar kashe wani fitaccen kwamandan kungiyar Boko Haram, Abu Rijab da wasu...

Yadda wani adalin direba ya kawo cigiyar haka maƙare a kuɗi

Wani direban motar kasuwa ya mayarwa rundunar ‘yan sandan jihar Kano jakar da ta bata dauke da makudan kudade.  Direban mai suna Safiyanu Mohammed...