An kashe mutane tare da yin garkuwa da wasu a Kebbi

An kashe mutane biyu yayin da aka yi garkuwa da wasu shida a karshen mako a lokacin da ‘yan bindiga suka kai hari kauyen Kwarikwarasa da ke karamar hukumar Maiyama a jihar Kebbi.

An tattaro cewa ‘yan bindigar sun mamaye al’ummar ne da sanyin safiyar Asabar domin kai harin.

Gwamnan jihar, Nasiru Idris, ya ziyarci al’ummar jihar inda ya tabbatar da cewa gwamnati ta tanadi matakan dakile sake afkuwar lamarin.

Ya ce gwamnatinsa ta bai wa jami’an tsaro dukkan goyon baya da hadin kan da ya kamata domin yakar miyagun ayyuka a fadin jihar.

“Ba za mu bar kokari ba har sai mun tabbatar da jihar sannan muka mayar da ita wurin da mutane za su kwana da idanuwansu biyu, su yi noman gonakinsu cikin lumana, su yi sana’o’insu na yau da kullum ba tare da wani tsoro ba,” inji gwamnan.

More News

Lauya ya nemi kotu ta bashi mako 4 ya nemo inda Yahaya Bello ya ɓuya

Abdulwahab Mohammed babban lauyan tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya nemi babbar kotun tarayya dake Abuja da ta bashi makonni huɗu domin ya...

Ɗalibai 9 aka tabbatar da yin garkuwa da su daga jami’an jihar Kogi

Gwamnatin jihar Kogi ta tabbatar da cewa ɗalibai 9 aka tabbatar sun ɓace bayan da wasu ƴan bindiga suka kai farmaki Jami'ar Kimiya da...

Mayaƙan Boko Haram Biyu Sun Miƙa Kansu Ga Sojoji

Aƙalla mayaƙan Boko Haram biyu ne suka miƙa kansu ga dakarun sojan Najeriya na rundunar Operation Haɗin Kai a yankin gabashin jihar Borno. Mayaƙan biyu...

Isa Dogonyaro Ɗan Majalisar Tarayya Daga Jihar Jigawa Ya Rasu

Isa Dogonyaro wakilin al'ummar ƙananan hukumomin Garki da Baɓura a majalisar wakilai ta tarayya ya rasu. Ɗaya daga cikin abokan aikin marigayin a majalisar tarayya,...