An kashe mutane tare da yin garkuwa da wasu a Kebbi

An kashe mutane biyu yayin da aka yi garkuwa da wasu shida a karshen mako a lokacin da ‘yan bindiga suka kai hari kauyen Kwarikwarasa da ke karamar hukumar Maiyama a jihar Kebbi.

An tattaro cewa ‘yan bindigar sun mamaye al’ummar ne da sanyin safiyar Asabar domin kai harin.

Gwamnan jihar, Nasiru Idris, ya ziyarci al’ummar jihar inda ya tabbatar da cewa gwamnati ta tanadi matakan dakile sake afkuwar lamarin.

Ya ce gwamnatinsa ta bai wa jami’an tsaro dukkan goyon baya da hadin kan da ya kamata domin yakar miyagun ayyuka a fadin jihar.

“Ba za mu bar kokari ba har sai mun tabbatar da jihar sannan muka mayar da ita wurin da mutane za su kwana da idanuwansu biyu, su yi noman gonakinsu cikin lumana, su yi sana’o’insu na yau da kullum ba tare da wani tsoro ba,” inji gwamnan.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]