An kashe mutane tare da yin garkuwa da wasu a Kebbi

An kashe mutane biyu yayin da aka yi garkuwa da wasu shida a karshen mako a lokacin da ‘yan bindiga suka kai hari kauyen Kwarikwarasa da ke karamar hukumar Maiyama a jihar Kebbi.

An tattaro cewa ‘yan bindigar sun mamaye al’ummar ne da sanyin safiyar Asabar domin kai harin.

Gwamnan jihar, Nasiru Idris, ya ziyarci al’ummar jihar inda ya tabbatar da cewa gwamnati ta tanadi matakan dakile sake afkuwar lamarin.

Ya ce gwamnatinsa ta bai wa jami’an tsaro dukkan goyon baya da hadin kan da ya kamata domin yakar miyagun ayyuka a fadin jihar.

“Ba za mu bar kokari ba har sai mun tabbatar da jihar sannan muka mayar da ita wurin da mutane za su kwana da idanuwansu biyu, su yi noman gonakinsu cikin lumana, su yi sana’o’insu na yau da kullum ba tare da wani tsoro ba,” inji gwamnan.

More News

An samu ambaliyar ruwa a Adamawa

Anguwan Tana, al’ummar karamar hukumar Yola ta Arewa, sun shiga tasgaro a ranar Alhamis sakamakon ambaliya daga kogin Kilange da kogin Faro. Mazaunan garin...

Sojoji sun ceto mutane 6 daga cikin ɗaliban jami’ar Gusau da aka sace

Sojoji sun ceto dalibai mata shida daga cikin daliban Jami'ar Gwamnatin Tarayya dake Gusau da aka bada rahoton yan bindiga sun yi garkuwa da...

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da ɗaliban Jami’ar Tarayya da ke Gusau

An sace wasu daliban jami’ar tarayya ta Gusau da ba a tantance adadinsu ba da sanyin safiyar Juma’a. ‘Yan ta’addan masu yawan gaske sun...

Ƴan sanda sun kama masu safarar makamai wa ƴan bindiga

Jami’an hukumar ‘yan sanda reshen Karasuwa a jihar Yobe sun cafke wasu mutane biyu da ake zargi da kai wa ‘yan bindiga makamai da...