An kashe mutane tare da yin garkuwa da wasu a Kebbi

An kashe mutane biyu yayin da aka yi garkuwa da wasu shida a karshen mako a lokacin da ‘yan bindiga suka kai hari kauyen Kwarikwarasa da ke karamar hukumar Maiyama a jihar Kebbi.

An tattaro cewa ‘yan bindigar sun mamaye al’ummar ne da sanyin safiyar Asabar domin kai harin.

Gwamnan jihar, Nasiru Idris, ya ziyarci al’ummar jihar inda ya tabbatar da cewa gwamnati ta tanadi matakan dakile sake afkuwar lamarin.

Ya ce gwamnatinsa ta bai wa jami’an tsaro dukkan goyon baya da hadin kan da ya kamata domin yakar miyagun ayyuka a fadin jihar.

“Ba za mu bar kokari ba har sai mun tabbatar da jihar sannan muka mayar da ita wurin da mutane za su kwana da idanuwansu biyu, su yi noman gonakinsu cikin lumana, su yi sana’o’insu na yau da kullum ba tare da wani tsoro ba,” inji gwamnan.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]