An kashe mutane 50 a Katsina

Mutum 50 ake fargabar an kashe sannan aka sace wasu da ba a san adadinsu ba sakamakon harin da ‘yan bindiga suka kai a jihar Katsina da ke arewacin Najeriya.

Mazauna garin Yargoje sun faɗa wa kamfanin labarai na Reuters cewa maharan sun afka wa ƙauyen ne tun ranar Lahadi da dare.

Gomman ‘yanfashi ne suka kutsa Æ™auyen da ke Æ™aramar hukumar Kankara, inda suka fara harbi a kan mai tsautsayi.

“Sun yi ta harbi a kan kowa da kowa, inda suka kashe mana mutum 50 ciki har da Æ™anina,” kamar yadda Hassan Ya’u ya bayyana ta waya.

Wani mazaunin Kankara mai suna Abdullahi Yunusa ya ce da kyar ya tsallake rijiya da baya, kuma hare-haren sun ci gaba har zuwa tsakar dare.

“Sun mayar da Æ™auyenmu wani filin kisa, kusan babu gidan da harin bai shafa ba,” in ji shi.

Mahukuntar jihar ba su ce komai ba zuwa lokacin haÉ—a wannan rahoton.

More News

Zanga-zanga: An jibge Æ´an sanda 4200 a Abuja

Rundunar Æ´an sandan birnin tarayya Abuja ta tura Æ´an sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haÆ™uri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...