An kashe mutane 50 a Katsina

Mutum 50 ake fargabar an kashe sannan aka sace wasu da ba a san adadinsu ba sakamakon harin da ‘yan bindiga suka kai a jihar Katsina da ke arewacin Najeriya.

Mazauna garin Yargoje sun faɗa wa kamfanin labarai na Reuters cewa maharan sun afka wa ƙauyen ne tun ranar Lahadi da dare.

Gomman ‘yanfashi ne suka kutsa ƙauyen da ke ƙaramar hukumar Kankara, inda suka fara harbi a kan mai tsautsayi.

“Sun yi ta harbi a kan kowa da kowa, inda suka kashe mana mutum 50 ciki har da ƙanina,” kamar yadda Hassan Ya’u ya bayyana ta waya.

Wani mazaunin Kankara mai suna Abdullahi Yunusa ya ce da kyar ya tsallake rijiya da baya, kuma hare-haren sun ci gaba har zuwa tsakar dare.

“Sun mayar da ƙauyenmu wani filin kisa, kusan babu gidan da harin bai shafa ba,” in ji shi.

Mahukuntar jihar ba su ce komai ba zuwa lokacin haɗa wannan rahoton.

More from this stream

Recomended