‘An kashe mutane 2,423, an yi garkuwa da 1,872 a cikin watanni takwas a karkashin Tinubu’

Gamayyar kungiyoyin farar hula a Najeriya karkashin inuwar kungiyar Civil Society Joint Action Group ta ce an kashe akalla mutane 2,423, yayin da aka sace 1,872 cikin watanni takwas na gwamnatin shugaba Bola Tinubu.

Da yake jawabi ga manema labarai a ranar Litinin a Abuja a madadin kungiyar, Auwal Musa Rafsanjani, ya yi kira ga shugaba Bola Tinubu da ya kafa dokar ta-baci kan garkuwa da mutane da sauran nau’o’in ta’addanci.

Ya ce lokaci ya yi da shugaban kasa zai bai wa jami’an tsaro da domin magance matsalar rashin tsaro.

An yi nuni da cewa wadannan nau’o’in rashin tsaro sun kawo cikas ga tsaro da walwalar ‘yan Nijeriya kuma suna ci gaba da tabarbarewa tsawon shekaru.

More News

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Majalisar dokokin Zamfara ta tsige kakakinta saboda tsanantar rashin tsaro a jihar

Majalisar dokokin jihar Zamfara ta tsige kakakinta, Bilyaminu Moriki, tare da nada Bashar Gummi, a matsayin kakakin majalisar. Hakan ya biyo bayan kudirin da dan...

Ƴan bindiga sun kashe mutane a Katsina

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina ta tabbatar da kisan mutane shida da wasu ‘yan bindiga suka yi a karamar hukumar Faskari a jihar. Jami’in hulda...

Sace-sacen motoci ya yawaita a Adamawa—Ƴan sanda

Ana ci gaba da samun karuwar sace-sacen motoci a jihar Adamawa, kamar yadda rundunar ‘yan sandan Najeriya ta tabbatar. Rundunar ‘yan sandan ta bayyana haka...