Wasu da ba a san ko suwaye ba sun kashe yar gidan, Bukar Abacha dan majalisar dokokin jihar Borno dake wakiltar mazabar Ngala.
Lamarin ya faru ne a gidan marigayiyar dake yankin Gidan Dembe dake Maiduguri babban birnin jihar.
Kamilu Sani, mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar shi ne ya tabbatar da faruwar lamarin a zantawar da yayi da jaridar The Cable a ranar Laraba.
Sani ya ce kawo yanzu basu tabbatar da wadanda suka aikata kisan kan ba.
Zagazola Makama dake wallafa bayanan sha’anin tsaro a yankin tafkin Chadi ya ce an samu gawar yar gidan dan majalisar hannayenta da kafafuwanta a daure ta baya a yayin da yarta mai shekara biyu take kuka a kusa da ita.