An kashe ƴar gidan wani ɗan majalisar dokokin jihar Borno

Wasu da ba a san ko suwaye ba sun kashe yar gidan, Bukar Abacha dan majalisar dokokin jihar Borno dake wakiltar mazabar Ngala.

Lamarin ya faru ne a gidan marigayiyar dake yankin Gidan Dembe dake Maiduguri babban birnin jihar.

Kamilu Sani, mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar shi ne ya tabbatar da faruwar lamarin a zantawar da yayi da jaridar The Cable a ranar Laraba.

Sani ya ce kawo yanzu basu tabbatar da wadanda suka aikata kisan kan ba.

Zagazola Makama dake wallafa bayanan sha’anin tsaro a yankin tafkin Chadi ya ce an samu gawar yar gidan dan majalisar hannayenta da kafafuwanta a daure ta baya a yayin da yarta mai shekara biyu take kuka a kusa da ita.

More News

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...

Sojoji sun lalata haramtattun matatun mai 32 a yankin Neja Delta

Dakarun sojan Najeriya na runduna ta 6 dake Fatakwal sun samu nasarar lalata haramtattun matatun man fetur 32 tare da ƙwace lita 250,000 na...

An gudanar da bikin cikar Kwankwaso shekara 68.

Tarin magoya baya da kuma abokanan siyasar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Kwankwaso ne suka halarci taron lakca da aka shirya domin bikin...

Faruk Lawan ya kammala zaman gidan yarin Kuje

An sako tsohon ɗan majalisar wakilai ta tarayya, Hon Faruk Lawan daga gidan yarin Kuje bayan da ya kammala zaman gidan yarin na shekaru...