Hukumar da ke kula da ‘yan gudun hijira da bakin haure ta kasa ta kaddamar da wasu gidaje sama da 40 da aka kammala saboda ‘yan gudun hijira a Zamfara.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da kakakin hukumar NCFRMI Tunde Oyasanya ya fitar ranar Litinin.
A jawabinsa yayin kaddamarwar, Mista Oyasanya ya ce Tijani Ahmed, kwamishinan tarayya na NCFRMI, ya ce aikin zai dawo da martaba jihar, da kuma farfado da mutane ga wadanda abin ya shafa.
Mista Ahmed ya ce magabatansa ne suka fara aikin na ‘yan gudun hijira da marasa galihu a fadin kasar inda shi kuma zai ƙara himma wajen aiwatarwa.