An kama wata mata dake safarar Tramadol zuwa kasar Turkiyya

Hukumar NDLEA dake yaki da masu sha da fataucin miyagun kwayoyi ta samu nasarar kama wata mata É—auke da kwayar Tramadol a filin jirgin saman Nnamdi Azikiwe dake Abuja.

Matar mai suna Lydia Lami Jatau an kama ta ne a filin jirgin saman Murtala Muhammad dake Lagos akan hanyarta ta zuwa birnin Istanbul na kasar Turkiyya.

Bincike da jami’an hukumar suka gudanar ya nuna cewar matar ta fito ne daga karamar hukumar Zangon Kataf ta jihar Kaduna kuma ta na zaune ne a birnin na Istanbul.

Femi Babafemi mai magana da yawun hukumar ta NDLEA ya ce matar ta bayyana cewa tayi haka ne domin ta biya kuɗin fansa har miliyan ₦5 na babarta da yan bindiga suka sace.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...