An kama wasu mutane biyu da hodar ibilis a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta sanar da kama wasu mutane biyu da aka samu ɗauke da ƙunshin hodar ibilis mai yawan gaske.

Mai magana da yawun rundunar ƴan sandan jihar, SP Benjamin Hundeyin shi ne ya bayyana haka cikin wani saƙo da ya wallafa shafinsa na X da aka fi sani da Twitter a baya.

Ya ce mutanen da aka kama sune Sunday Nwabufor mai shekaru 47 mazaunin unguwar FESTAC da kuma Obinna Nweke mai shekaru 45 mazaunin unguwar Ketu dake yankin Mile 12.

Jami’an Æ´an sandan daga ofishin Æ´an sanda na Ojo ne suka kama mutanen a ranar 18 ga watan Satumba biyo bayan wasu bayanai da suka samu akan mutanen.

Ƙulli 120 aka same su da shi a yayin da ake cigaba da gudanar da bincike.

More News

Ƴan sanda sun kama wani mutum ɗauke da bindigogi 20 a Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce jami'anta sun kama wani  riÆ™aƙƙen mai safarar bindiga inda aka same shi da bindigogin AK-47 Æ™irar gida...

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waÉ—anda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...