An kama wani shugaban PDP a Zamfara da laifin shigo da makamai

Dakarun rundunar hadin gwiwa ta Operation Hadarin Daji sun kama wasu mutane uku da ake zargin ‘yan bindiga ne a jihar Zamfara.

Daya daga cikin wadanda ake zargin, Aminu Ibrahim, an ce shugaban jam’iyyar PDP na gundumar Birnin Yero a karamar hukumar Shinkafi.

PRNigeria ta tattaro daga wata majiyar leken asiri ta soji a jihar cewa an kama Ibrahim, tare da abokan sa, wato Musa Usman Seun da Isah Mohammed a ranar Litinin.

Majiyar ta ci gaba da cewa: “Dakarun rundunar hadin gwiwa ta shiyyar Arewa maso Yamma Operation HADARIN DAJI da suke aiki da sahihan bayanan sirri kan ayyukan wani fitaccen dan bindiga da nufin fasa kwaurin makamai zuwa cikin jihar Zamfara, nan take sojojin suka tare hanyar tare da cafke wasu mutane 3 da ake zarginsu da aikatawa.

“Mutane 3 da ake zargin sun hada da Musa Usman Seun, Aminu Ibrahim, da Isah Mohammed an kama su ne kwanan nan a Shinkafi a ranar 22 ga watan Junairu 2024 kuma an kwato kudi naira miliyan biyu da dubu dari biyar da tamanin, Volkswagen Wagon 1, wayoyin hannu 3 da sauran kayayyaki.”

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...