An kama wani shugaban PDP a Zamfara da laifin shigo da makamai

Dakarun rundunar hadin gwiwa ta Operation Hadarin Daji sun kama wasu mutane uku da ake zargin ‘yan bindiga ne a jihar Zamfara.

Daya daga cikin wadanda ake zargin, Aminu Ibrahim, an ce shugaban jam’iyyar PDP na gundumar Birnin Yero a karamar hukumar Shinkafi.

PRNigeria ta tattaro daga wata majiyar leken asiri ta soji a jihar cewa an kama Ibrahim, tare da abokan sa, wato Musa Usman Seun da Isah Mohammed a ranar Litinin.

Majiyar ta ci gaba da cewa: “Dakarun rundunar hadin gwiwa ta shiyyar Arewa maso Yamma Operation HADARIN DAJI da suke aiki da sahihan bayanan sirri kan ayyukan wani fitaccen dan bindiga da nufin fasa kwaurin makamai zuwa cikin jihar Zamfara, nan take sojojin suka tare hanyar tare da cafke wasu mutane 3 da ake zarginsu da aikatawa.

“Mutane 3 da ake zargin sun hada da Musa Usman Seun, Aminu Ibrahim, da Isah Mohammed an kama su ne kwanan nan a Shinkafi a ranar 22 ga watan Junairu 2024 kuma an kwato kudi naira miliyan biyu da dubu dari biyar da tamanin, Volkswagen Wagon 1, wayoyin hannu 3 da sauran kayayyaki.”

More News

Ƴan Fashin Daji Sun Kashe Mutane 7 A Jihar Kebbi

Mutane 7 aka bada rahoton ƴan fashin daji sun kashe  a garin Tudun Bici dake ƙaramar hukumar Danko Wasagu ta jihar Kebbi. A cewar mazauna...

Tsoffin gwamnoni sun wawashe sama da naira tiriliyan 2 tun komawa dimokuraɗiyya

Aƙalla tsoffin gwamnoni 58 ne ake zargin sun wawure kuma sun yi almubazzarancin jimillar naira Tiriliyan 2.187 a cikin shekaru 25 tun komawa mulkin...

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...