An kama wani mutumi mai lalata da ƙananan yara

Rundunar ‘yan sandan jihar Abia ta kama wani mutum mai shekaru 37, Anumudu Chigozie wanda mazaunin kauyen Umuobiokwa ne bisa zarginsa da aikata laifin lalata da kananan yara.

An kama Chigozie, wanda a baya ya yi aiki a matsayin ma’aikacin jirgin sama (OAP) tare da kafafen yada labarai a jihar, jami’an rundunar ‘yan sandan yankin Gabashin Ngwa na rundunar ‘yan sandan jihar Abia ne suka kama shi, biyo bayan rahoton da aka kai musu.

Kodayake rundunar ‘yan sanda ba ta bayyana cikakken bayanin kama shi da laifin da ya aikata ba, sai dai kawai mai magani da yawun rundunar ‘yan sandan jihar Abia ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce za a gurfanar da shi gaban kotu bayan bincike na gaskiya.

More News

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...

Wasu ɗaliban Jami’ar Jihar Nasarawa sun mutu a lokacin turmutsutsin karɓar tallafin abinci

Dalibai biyu daga Jami’ar Jihar Nasarawa da ke Keffi (NSUK) sun rasa rayukansu a wani turmutsitsi da ya barke a lokacin da suke kokarin...

Jarumin Nollywwood, Mr. Ibu, ya rasu

Jarumin Nollywood, John Okafor, wanda aka fi sani da "Mr Ibu", ya rasu yana da shekaru 62. Emeka Rollas, shugaban kungiyar Actors Guild of Nigeria,...

Miyetti Allah ta nemi a cafke Sunday Igboho saboda barazanar yaƙar Fulani

Kungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria, MACBAN, ta yi kira da a damke wani dan kabilar Yarbawa, Sunday Adeyemo, wanda aka fi...