An kama wani Fasto da laifin kashe matarsa har Lahira

Rundunar ‘yan sanda a jihar Ekiti ta kama wani fasto na cocin Christ Apostolic Church, Abiodun Sunday, bisa zargin kashe matarsa.

Kakakin Rundunar ’Yan sandan Jihar Ekiti, DSP Sunday Abutu, ya tabbatar da kisan matar Fasto, Tosin Oluwadere, a Ido-Ile a karamar Hukumar Ekiti ta Yamma ta Jihar Ekiti a ranar Alhamis.

Kakakin ‘yan sandan ya kuma bayyana cewa wanda ake zargin yana hannun ‘yan sanda kuma ana ci gaba da gudanar da bincike kan kisan.

An tattaro cewa wanda ake zargin limamin coci ne kuma likitan gargajiya.

Wani dan’uwan mamaciyar, Mista Samuel Ibironke, ya yi zargin cewa, “Bayan ya kashe ƙanwata, sai ya kira matata wadda ma’aikaciyar lafiya ce ta zo ta taimake shi, sai matata ta isa wurin ta gano cewa ya shake kanwata har lahira.”

More News

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...

Wasu ɗaliban Jami’ar Jihar Nasarawa sun mutu a lokacin turmutsutsin karɓar tallafin abinci

Dalibai biyu daga Jami’ar Jihar Nasarawa da ke Keffi (NSUK) sun rasa rayukansu a wani turmutsitsi da ya barke a lokacin da suke kokarin...

Jarumin Nollywwood, Mr. Ibu, ya rasu

Jarumin Nollywood, John Okafor, wanda aka fi sani da "Mr Ibu", ya rasu yana da shekaru 62. Emeka Rollas, shugaban kungiyar Actors Guild of Nigeria,...

Miyetti Allah ta nemi a cafke Sunday Igboho saboda barazanar yaƙar Fulani

Kungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria, MACBAN, ta yi kira da a damke wani dan kabilar Yarbawa, Sunday Adeyemo, wanda aka fi...