An Kama Wani Shugaban Karamar Hukuma Da Ya Shirya Kashe Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Benue

Rundunar yan sandan Najeriya ta sanar da kama wani shugaban karamar hukuma a jihar Benue da kuma wani mutum guda inda ake zarginsu da kitsa kisan kai.

Rundunar ta ce ta samu nasarar kama mutanen biyu ne saboda Æ™oÆ™arin jami’anta.

A wata sanarwa mai magana da yawun rundunar, ACP Olumuyiwa Adejobi ya ce binciken farko da suka gudanar ya nuna cewa shugaban karamar hukumar ya yi hayar wasu yan bindiga da niyar su hallaka shugaban majalisar dokokin jihar Benue, Hon. Aondona Hycenth Dajoh.

Adejobi ya ce biyo bayan samun kwararan bayanan sirri sashen tattara bayanan sirri da kuma rundunar kar ta kwana sun kama aiki gadan-gadan har ta kai ga kama mutanen biyu.

Kawo yanzu mutanen biyu na tsare a hedkwatar rundunar yan sandan inda suke cigaba da amsa tambayoyi.

More News

Gwamnatin Adamawa Ta Ƙara Hutun Ɗaliban Makarantu Saboda Annobar Cutar Ƙyanda

Gwamnatin jihar Adamawa ta tsawaita lokacin komawar É—aliban jihar makarantunsu domin fara  zangon karatu na uku saboda annobar cutar Æ™yanda. A wata sanarwa ranar Litinin,...

Sojan Jamhuriyar Nijar sun kama Gawurtaccen ÆŠan Fashin dajin Najeriya Kachalla Mai Daji

Dakarun sojan Jamhuriyar Nijar sun samu nasara kama gawurtaccen É—an fashin dajin nan mai suna Kachalla Mai Daji a garin Illela dake kan iyakar...

Ƴan Fashin Daji Sun Kashe Mutane 7 A Jihar Kebbi

Mutane 7 aka bada rahoton ƴan fashin daji sun kashe  a garin Tudun Bici dake ƙaramar hukumar Danko Wasagu ta jihar Kebbi. A cewar mazauna...

Tsoffin gwamnoni sun wawashe sama da naira tiriliyan 2 tun komawa dimokuraÉ—iyya

Aƙalla tsoffin gwamnoni 58 ne ake zargin sun wawure kuma sun yi almubazzarancin jimillar naira Tiriliyan 2.187 a cikin shekaru 25 tun komawa mulkin...