[ad_1]
Rundunar Æ´ansandan Najeriya ta samu nasarar kama gungun wasu yan fashi da makami da kuma masu garkuwa da mutane.
Yan fashin suna gudanar da mummunan sana’ar tasu akan hanyar Kano-Kaduna-Abuja.
Bata garin na amfani ne da kayan sojoji wajen yin fashi da makami da kuma garkuwa da mutane.
Mataimakin kwamishinan Æ´ansanda, Abba Kyari shine ya jagoranci kama su.
Mutanen sun amince da yin garkuwa da mutane tare da kashe wasu mutanen da dama akan hanyar Kano zuwa Kaduna da kuma Kaduna zuwa Abuja.
Kayayyaki da aka samu a wurinsu sun hada da kakin sojoji, bindigogi biyu kirar Ak-47.
Hanyar Abuja zuwa Kaduna ta zama wata matattarar masu garkuwa da mutane inda hakan yake jefa fargaba da tsoro ga matafiya dake bi ta hanyar.
A lokuta da dama wasu matafiya dake zuwa Abuja na shiga jirgin kasa daga Kaduna.
[ad_2]