An kama likitan bogi a Jihar Filato

Kungiyar likitocin Najeriya reshen jihar Filato a ranar Laraba ta ce ta kama wani likitan bogi bisa zarginsa da gudanar da aikin jinya a makarantu da wuraren ibada a jihar.

Shugaban NMA na jihar, Dokta Bapigaan Audu, ne ya bayyana hakan a ranar Laraba a wata sanarwa da ya sanya wa hannu tare da jami’in hulda da jama’a na kungiyar, Dokta Istifanus Bako.

A cewar NMA, wanda ake zargin ya yi amfani da sunaye daban-daban wajen gudanar da wannan aika-aika.

An kama shi ne a babban birnin Jos bayan wani bincike da kungiyar ta kaddamar tare da jami’an ma’aikatar lafiya ta jihar.

An tattaro cewa daga bisani an garzaya da wanda ake zargin zuwa hedikwatar ‘yan sanda da ke Jos inda aka tsare shi.

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...