An Kama Barayin Kare Da Agwagwi A Kano

Jami’an tsaron bijilante dake unguwar Gurungawa a karamar hukumar Kumbotso ta jihar Kano sun kama wasu mutane hudu da ake zargi da satar karnuka da kuma agwagwi.

Kwamandan bijilante na garin, Abdulhamid Dan-Azumi ya ce jami’ansa sun ji mostin mutanen da misalin karfe uku na dare lokacin da suka ji karnuka na haushi kuma wadanda da ake zargin sun samu nasarar kashe daya daga cikin karnuka.

Ya lissafa wadanda da ake zargi da suka hada da Sunusi Muhammad Abubakar, Sulaiman Baffa da Buhari Adamu, dukkaninsu mazauna unguwar Sheka da kuma Walid Ishak dake unguwar Gandun Albasa.

Kwamandan ya ce ” Bayan da muka kama su mun gano cewa sun dade suna aikata haka. Daya daga cikin su an san shi da satar kare yana turawa kudancin kasarnan.

“Mun kuma gano makamai a hannunsu za mu mika su hannun jami’an yan sanda.”

More News

Tinibu ya aikawa da majalisar dattawa sunaye 7 na  ministocin da zai naÉ—a

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya yi kira ga majalisar dattawa da ta tabbatar da sunayen mutane 7 da ya tura majalisar da zai...

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...

Sojoji sun lalata haramtattun matatun mai 32 a yankin Neja Delta

Dakarun sojan Najeriya na runduna ta 6 dake Fatakwal sun samu nasarar lalata haramtattun matatun man fetur 32 tare da ƙwace lita 250,000 na...

An gudanar da bikin cikar Kwankwaso shekara 68.

Tarin magoya baya da kuma abokanan siyasar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Kwankwaso ne suka halarci taron lakca da aka shirya domin bikin...