An kama ɓarayin wayoyin wutar lantarki a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna ta ce jami’anta sun kama wasu mutane uku da ake zargi da sace igiyoyin wutar lantarki a garin Saminaka da ke karamar hukumar Lere a jihar.

Kakakin rundunar ‘yan sandan, ASP Mansir Hassan, ya bayyana hakan a ranar Lahadi a Kaduna.

Hassan ya ce da misalin karfe 0400 na ranar Lahadi, rundunar ta samu bayanai game da sace-sacen da aka yi a wani gida a kan titin Kafanchan, cikin garin Saminaka, an ga wasu da ba a san ko su waye ba dauke da wasu igiyoyin wutar lantarki.

“An kai tawagar mu ‘yan sintiri zuwa yankin, kuma an kama mutanen uku da suka fito daga Unguwar Ungwan Bawa na garin,” in ji shi.

More News

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...

Wasu ɗaliban Jami’ar Jihar Nasarawa sun mutu a lokacin turmutsutsin karɓar tallafin abinci

Dalibai biyu daga Jami’ar Jihar Nasarawa da ke Keffi (NSUK) sun rasa rayukansu a wani turmutsitsi da ya barke a lokacin da suke kokarin...

Jarumin Nollywwood, Mr. Ibu, ya rasu

Jarumin Nollywood, John Okafor, wanda aka fi sani da "Mr Ibu", ya rasu yana da shekaru 62. Emeka Rollas, shugaban kungiyar Actors Guild of Nigeria,...

Miyetti Allah ta nemi a cafke Sunday Igboho saboda barazanar yaƙar Fulani

Kungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria, MACBAN, ta yi kira da a damke wani dan kabilar Yarbawa, Sunday Adeyemo, wanda aka fi...