An kama ƴan kungiyar IPOB 18 da ake zargi da kisan ƴan sanda

Rundunar yan sandan jihar Imo ta kama mutane 18 da ake zargi da zama yan kungiyar IPOB da suke da hannu a kisan ƴan sanda biyu a mahadar Ahiara dake karamar hukumar Ahiazu-Mbaise ta jihar.

Jami’an tsaron da suka tsaya shan mai a gidan man BOEK Petroleum a ranar Litinin sun fuskanci farmaki daga wasu ƴan bindiga da ake zargin ƴan IPOB ne.

Maharan na sanye ne da kayan sojoji inda suka farma ƴan sandan babu zato dake motoci uku kuma suka riƙa harbin kan me uwa da wabi.

A cewar Henry Okoye mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar ya ce yan sandan biyu da aka kashe a harin sun haɗa da DPO na Ahiazu-Mbaise da kuma wani insifecta.

Ya ce mutanen na cigaba da amsa tambayoyi a yayin da ake cigaba da bincike.

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...