
Hakkin mallakar hoto
Getty Images
Sarkin yana cikin ‘koshin lafiya bayan harin’
Wasu mahara sun kai wa Sarkin Potiskum, Alhaji Umaru Bubaram, hari inda suka kashe mutum shida, kamar yadda rundunar ‘yan sanda a jihar Kaduna ta bayyana.
Kakakin Rundunar ‘Yan sanda a jihar Kaduna DSP Yakubu Abubakar Sabo ya tabbatar wa da BBC faruwar al’amarin.
DSP Sabo ya ce abin ya faru ne a kan hanyar Kaduna zuwa Zariya, a kusa da garin Marabar Jos.
Ya ce wasu mahara ne suka bude wa ayarin motocin sarkin wuta wanda hakan ya yi ajalin mutum shida – biyu fasinjoji da ke tafiya a hanyar, hudu kuma daga cikin jama’ar sarkin.
Mun tuntubi diyar sarkin Fatsima Umar kuma ta shaida mana cewa dogaransa uku ne suka mutu da kuma wani direbansa daya.
Kuma ta ce sarkin yana cikin koshin lafiya tun bayan faruwar al’amarin.