An kaddamar da dokar jefe ‘yan luwadi a Brunei

Kasar Brunei za ta fara aiwatar da shari’ar musulunci inda za a fara kashe ‘yan luwadi da
ma’aurata mazinata.

Sabuwar dokar waddda za ta fara aiki a ranar Laraba, ta hada da sauran laifuka wadanda suka
hada da yanke hannu.

Lamarin ya ja Allah wadai daga kasashen ketare. ‘Yan luwadin kasar sun bayyana damuwa da
sabuwar dokar. “Ka wayi gari kaga makwabtanka, ‘yan uwanka, da danginka suna tunanin cewa kai ba mutum bane kuma ya kamata a jefe ka”, a cewar wani dan luwadi dake zaune a kasar wanda ya nemi BBC ta sakaya sunansa.

Sarkin kasar, wadda take a kudu maso gabashin Asiya na nema a kara tabbatar da “koyarwa ta
addinin musulunci.” Ina fatan ganin koyarwar addinin muslunci ta karu a kasar nan a cewar Sarki Hassanal Bolkiah a cewar kamfani dillancin labarai ta AFP.

Luwadi laifi ne a kasar kuma ana hukunta masu laifin da hukuncin shekara 10 a gidan kaso. Musulmai ne kashi biyu cikin uku na mutanen kasar mai mutane 420,000.

Akwai hukuncin kisa a kasar amma ba a kashe kowa ba tun 1957.

More News

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waÉ—anda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...

Mutane 18 sun ƙone ƙurmus a wani hatsarin mota

Aƙalla fasinjoji 18 ne suka ƙone ƙurmus a wani hatsarin mota da ya faru akan babbar hanyar Ojebu-Ode zuwa Ore a yankin Ogbere dake...