An gano mai cutar Korona da ya tsere a jihar Borno – AREWA News

An gano daya daga cikin masu cutar Korona da suka tsere a jihar Borno. Kwamishinan lafiya na jihar, Salisu Kwayabura shi ne ya tabbatar da haka.

Kwayabura ya bayyana haka ne cikin wani sako da ya wallafa ranar Litinin a shafin Facebook na gwamnatin jihar.

Ya ce an gano Abbas Kaka Hassan mai shekaru 24 da misalin karfe biyu na dare a Maiduguri.

Hukumomi a jihar sun bayyana bacewar Hassan tare da wata mata da aka yi musu gwaji tare a asibitin koyarwa na jami’ar Maiduguri bayan da ya kashe wayarsa da kuma ta mahaifiyarsa.

Kwamishinan ya ce an gano marar lafiyar ne a gidansu inda aka same shi cikin mawuyacin hali kuma tuni aka dauke shi ya zuwa cibiyar da ake killace masu cutar Korona a jihar inda yake numfashi da taimakon na’ura.

More News

Tayoyin jirgin saman Max Air sun fashe a Yola

Jirgin saman kamfanin Max Air ƙirar Boeing 737 mai rijistar namba 5N-ADB dake ɗauke da fasinjoji 118 da ma'aikata 6 ya gamu da matsala...

Ɗan majalisar wakilai ta tarayya ya mutu

Hon. Olaide Akinremi Jagaba mamba a majalisar wakilai ta Najeriya dake wakiltar mazaɓar Ibadan North a majalisar ya mutu. Kawo yanzu babu cikakken bayani kan...

Gwamnan Kano ya sanya hannu kan dokar yin gwajin lafiya kafin aure

Gwamnan jihar Kano, Engr Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan wata doka za ta tilastawa masu yin aure yin wasu gwaje-gwajen lafiya gabanin...

An kashe kwamandan soji a Katsina

An kashe kwamandan sojoji na wani sansanin soji da ke Sabon Garin Dan’Ali a karamar hukumar Danmusa a jihar Katsina a wani harin kwantan...