An gano mai cutar Korona da ya tsere a jihar Borno – AREWA News

An gano daya daga cikin masu cutar Korona da suka tsere a jihar Borno. Kwamishinan lafiya na jihar, Salisu Kwayabura shi ne ya tabbatar da haka.

Kwayabura ya bayyana haka ne cikin wani sako da ya wallafa ranar Litinin a shafin Facebook na gwamnatin jihar.

Ya ce an gano Abbas Kaka Hassan mai shekaru 24 da misalin karfe biyu na dare a Maiduguri.

Hukumomi a jihar sun bayyana bacewar Hassan tare da wata mata da aka yi musu gwaji tare a asibitin koyarwa na jami’ar Maiduguri bayan da ya kashe wayarsa da kuma ta mahaifiyarsa.

Kwamishinan ya ce an gano marar lafiyar ne a gidansu inda aka same shi cikin mawuyacin hali kuma tuni aka dauke shi ya zuwa cibiyar da ake killace masu cutar Korona a jihar inda yake numfashi da taimakon na’ura.

More News

Ƴan bindiga sun ƙone ginin hedkwatar ƙaramar hukuma tare da kashe jami’an tsaro

Ƴan bindiga sun kai farmaki hedkwatar ƙaramar hukumar, Isiala Mbano dake jihar Imo da tsakar daren ranar 3 ga watan Satumba inda suka ƙone...

An kama wasu ƴanta’adda da ke da alaƙa da Turji

Akalla mayaka 18 da ke da alaka da fitaccen shugaban ‘yan ta’adda Bello Turji aka kama a jihar Sokoto da ke arewa maso yammacin...

Dakarun Najeriya sun kai farmaki wa ƴan’adda a Borno, wani kwamanda ya miƙa wuya

Rundunar sojin Najeriya ta sanar a ranar Lahadin cewa dakarunta sun yi nasarar kashe wani fitaccen kwamandan kungiyar Boko Haram, Abu Rijab da wasu...

Yadda wani adalin direba ya kawo cigiyar haka maƙare a kuɗi

Wani direban motar kasuwa ya mayarwa rundunar ‘yan sandan jihar Kano jakar da ta bata dauke da makudan kudade.  Direban mai suna Safiyanu Mohammed...