An Fara Yin Rijistar Marasa Aikin Yi A Sokoto

Hukumar NDE dake samar da aikin yi a Najeriya ofishin jihar Sokoto ya fara yin rijistar mara sa aikin yi a jihar da suka fito daga kananan hukumomin jihar 23.

Shugaban sashen tsare-tsare,bincike da kuma kididdiga na hedkwatar hukumar dake Abuja, Mallam Umar Aliyu shi ne ke sanya ido kan shirin tare da Sulaiman Adamu Kangiwa wakilin shugaban shirin a jihar.

Ana gudanar da aikin yin rijistar ne a ofishin hukumar ta NDE dake jihar da kuma a kananan hukumomi 23 na jihar.

Da suke zagawa domin ganin yadda shirin ke gudana jami’an su bayyana gamsuwar su kan yadda shirin ke gudana ba tare da wasu matsaloli ba.

An dai fara shirin ne a ranar 17 ga watan Afrilu inda za kuma a kammala ranar 9 ga watan Mayu.

More News

Wani sojan ruwan Najeriya ya hallaka abokin aikinsa a Zamfara

Hedikwatar Tsaron Najeriya ta kama wani sojan ruwa mai suna A. Akila bisa zarginsa da kashe abokin aikinsa.An tura Akila zuwa sansanin Forward Operating...

Kotu ta bada umarnin gudanar da zaɓen ƙananan hukumomi a Kano

Wata babbar kotu a jihar Kano ta umarci hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar wato KANSIEC da ta cigaba da shirye-shiryen gudanar da...

Kotu ta bada umarnin gudanar da zaɓen ƙananan hukumomi a Kano

Wata babbar kotu a jihar Kano ta umarci hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar wato KANSIEC da ta cigaba da shirye-shiryen gudanar da...

Ministan tsaro Badaru ya yaba wa gwamnan Zamfara saboda tallafa wa aikin soji a jihar

Ministan Tsaro, Mohammed Abubakar Badaru, ya jinjina wa Gwamna Dauda Lawal bisa jajircewarsa da ci gaba da tallafa wa ayyukan soji a Jihar Zamfara.Ministan...