An fara tattara sakamakon zaɓe a jihar Imo

Hukumar zabe mai zaman kanta ta fara tattara sakamakon zaben gwamnan jihar Imo.

An fara gudanar da aikin ne karkashin jagorancin jami’in tattara sakamako Farfesa Abayomi Fasina, mataimakin shugaban jami’ar tarayya da ke Oye, Ekiti, da misalin karfe 2:40 na safiyar ranar Lahadi a cibiyar tattara bayanai da ke Owerri, babban birnin jihar.

Ana tattara sakamakon zaben ne sa’o’i kadan bayan zaben gwamna, daya daga cikin zabuka uku da aka gudanar a kasar ranar Asabar.

A halin da ake ciki, faifan bidiyo da ke zagayawa a shafukan sada zumunta sun nuna wakilan jam’iyyar suna nuna rashin amincewarsu da saurin tattara sakamako a wurin taron.

Ana iya jin ɗaya daga cikin wakilai a cikin bidiyon yana cewa “Ina muke gaggawar zuwa?”

Gwamna Hope Uzodimma na jam’iyyar All Progressives Congress ya sake tsayawa takara.

Athan Achonu na jam’iyyar Labour da Samuel Anyanwu na jam’iyyar Peoples Democratic Party su ne manyan ‘yan takara biyu.

More News

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...

Wasu ɗaliban Jami’ar Jihar Nasarawa sun mutu a lokacin turmutsutsin karɓar tallafin abinci

Dalibai biyu daga Jami’ar Jihar Nasarawa da ke Keffi (NSUK) sun rasa rayukansu a wani turmutsitsi da ya barke a lokacin da suke kokarin...

Jarumin Nollywwood, Mr. Ibu, ya rasu

Jarumin Nollywood, John Okafor, wanda aka fi sani da "Mr Ibu", ya rasu yana da shekaru 62. Emeka Rollas, shugaban kungiyar Actors Guild of Nigeria,...

Miyetti Allah ta nemi a cafke Sunday Igboho saboda barazanar yaƙar Fulani

Kungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria, MACBAN, ta yi kira da a damke wani dan kabilar Yarbawa, Sunday Adeyemo, wanda aka fi...