An fara rushe wasu gine-gine 500 a kasuwar Karmo dake Abuja

Hukumar FCTA dake kula da birnin tarayya Abuja ta fara rushe gine-gine sama da 500 da aka yi ba bisa ka’ida ba a kasuwar Karmo dake Abuja.

Mukhtar Galadima daraktan sashen dake kare birnin daga bunÆ™asa ba tare da tsari ba ya ce an fara rushe-rushen ne biyo bayan Æ™arewar wa’adin awanni 24 da aka bawa Æ´an kasuwar na su tashi daga wurin.

Galadima wanda ya samu wakilcin Garba Jibril mataimakin darakta dake lura da yankin Karmo da sauran wasu yankuna ya ce an sanar da dukkan mutanen da abun ya shafa inda ya Æ™ara da cewa anbi dukkanin wata ka’ida kafin a fara aikin.

“A fili yake Æ™arara mutane suna shafe a wanni kafin su wuce ta titin  musamman ranar da kasuwa take ci,” ya ce.

“Domin shawo kan wannan matsalar ministan Abuja Nyesom Wike ya bayar da umarnin rushe gine-gine da aka yi ba bisa ka’ida ba,” ya ce.

Galadima ya yi kira ga Æ´an kasuwar da abun ya shafa da su koma kasuwannin da aka samar .

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya Æ™irÆ™iri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a Æ™ara wa Æ´an bautar Æ™asa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...