An dakatar da sarkin da ya naɗa dan ta’adda Sarauta a Zamfara

Gwamnan jihar Zamfara, Bello Matawalle ya dakatar da Sarkin Birnin Yandoto a karamar hukumar Tsafe ta jihar,Alhaji Aliyu Marafa bayan da ya naɗa wani kasurgumin dan bindiga, Ado Aleiro sarauta.

An naɗa Aleiro sarautar Sarkin Fulani a ranar Asabar.

A cewar sarkin an naɗa, Aleiro sarautar ne sakamakon rawar da ya taka wajen sulhun zaman lafiya tsakanin masarautar da kuma yan bindigar da suke addabar karamar hukumar Tsafe.

Amma kuma a wata sanarwa da sakataren gwamnatin jihar, Kabiru Balarabe Sardauna ya fitar gwamnatin ta nesanta kanta daga nadin sarautar da aka yi inda ta sanar da dakatarwar da gaggawa.

Tuni dai aka naɗa hakimin Yandoto, Alhaji Mahe Marafa domin ya cigaba da jagorantar masarautar.

More News

Ribadu ya koka kan yadda jami’an tsaro suke sayarwa da ƴan ta’adda bindigogi

Mai bawa shugaban shawara kan harkokin tsaro, Mallam Nuhu Ribadu ya ce wasu daga jami'an ƴan sanda da kuma sojoji suna ɗaukar bindigogi daga...

Gwamnan Legas Sanwo-Olu ya kara mafi ƙarancin albashi zuwa naira 85,000

Gwamnan Jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu, ya bayyana shirin gwamnatinsa na fara biyan sabon mafi karancin albashi na N85,000 ga ma'aikatan jihar.Sanwo-Olu ya bayyana hakan...

Sama da mutane 100 aka tabbatar sun mutu a gobarar hatsarin tankar mai a Jigawa

Rundunar ƴan sandan jihar Jigawa ta tabbatar da mutuwar mutane 140 a hatsarin gobarar tankar mai da ta faru a garin Majia dake kan...

Sojoji sun kashe ɗan Boko Haram a Borno

Dakarun rundunar sojan Najeriya na Birged Ta 21 dake aiki da rundunar Operationa Haɗin Kai dake aikin samar da tsaro a yankin arewa maso...