An dage ƙidayar jama’a ta 2023

An dage kididdigar yawan jama’a ta 2023, wadda aka shirya gudanarwa tun daga ranar 3 zuwa 7 ga Mayu, 2023, kuma gwamnati mai zuwa za ta tsayar da wata sabuwar rana.

Gwamnatin Tarayya ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ma’aikatar yada labarai da al’adu ta fitar ta shafinta na Twitter.

Sanarwar ta ce, “Shugaba Muhammadu Buhari ya amince da dage kididdigar yawan jama’a da gidaje na shekarar 2023, wanda tun farko aka shirya gudanarwa daga 3-7 ga Mayu 2023, zuwa ranar da gwamnati mai zuwa za ta tsayar da rana.

“Shugaban ya amince da hakan ne bayan ganawa da wasu mambobin majalisar zartarwa ta tarayya da shugaban @natpopcom da tawagarsa a fadar shugaban kasa da ke Abuja ranar Juma’a 28 ga Afrilu 2023.”

More News

Ɗan ta’addar Boko Haram ya miƙa kansa ga sojoji

Alhaji Wosai wani mamba a ƙungiyar ƴan ta'addar Boko Haram ya miƙa kansa ga dakarun sojan Najeriya na rundunar Operation Haɗin Kai. Rahotanni sun bayyana...

An kuɓutar da wasu ɗaliban da aka sace a jami’a a Kogi

Rundunar ‘yan sandan jihar Kogi ta bayyana cewa an ceto 14 daga cikin daliban jami’ar kimiyya da fasaha ta Confluence da ke Osara Okene...

Hukumar NMDPRA ta rufe wani gidan mai da ya karkatar da tankar man fetur 18

Hukumar NMDPRA dake lura da tacewa tare rarraba man fetur da iskar gas ta rufe gidan man Botoson Oil and Gas LTD dake jihar...

Jirgin saman kamfanin Xejet ya zame daga kan titin filin jirgin saman Lagos

A ranar Asabar ne wani jirgin sama mallakin kamfanin Xejet ya zame daga kan titin filin jirgin saman Murtala Muhammad dake Lagos. Hukumar NSIB dake...