Jami’ar Tarayya ta Gusau da ke jihar Zamfara ta bayar da sanarwar cewa ya zuwa yanzu an ceto ɗalibai 14 da leburori biyu waɗanda ƴan bindiga suka awon-gaba da su a daren Juma’ar da ta gabata.
Cikin wata sanarwa da jami’ar ta fitar, na cewa a jimilla, an kuɓutar da mutum 16, 14 dalibai, 2 kuma ma’aikata tun bayan sace su da aka yi.
Jami’ar ta kara da cewa waɗanda suka shiga firgici a hannun ƴan bindigar, tuni aka haɗa su da iyalansu.
Haka nan sanarwar ta buƙaci ɗalibai da malaman jami’ar su ci gaba da tafiyar da lamurransu kamar yadda suka saba.
Ta kuma yaba wa jami’an tsaron Najeriya bisa ƙoƙarin da suka yi na ƙwato waɗanda aka sace.