An ceto ɗaliban jami’ar Zamfara guda 14 da ƴan bindiga suka sace

Jami’ar Tarayya ta Gusau da ke jihar Zamfara ta bayar da sanarwar cewa ya zuwa yanzu an ceto ɗalibai 14 da leburori biyu waɗanda ƴan bindiga suka awon-gaba da su a daren Juma’ar da ta gabata.

Cikin wata sanarwa da jami’ar ta fitar, na cewa a jimilla, an kuɓutar da mutum 16, 14 dalibai, 2 kuma ma’aikata tun bayan sace su da aka yi.

Jami’ar ta kara da cewa waɗanda suka shiga firgici a hannun ƴan bindigar, tuni aka haɗa su da iyalansu.

Haka nan sanarwar ta buƙaci ɗalibai da malaman jami’ar su ci gaba da tafiyar da lamurransu kamar yadda suka saba.

Ta kuma yaba wa jami’an tsaron Najeriya bisa ƙoƙarin da suka yi na ƙwato waɗanda aka sace.

More News

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Wasu ɗaliban Jami’ar Jihar Nasarawa sun mutu a lokacin turmutsutsin karɓar tallafin abinci

Dalibai biyu daga Jami’ar Jihar Nasarawa da ke Keffi (NSUK) sun rasa rayukansu a wani turmutsitsi da ya barke a lokacin da suke kokarin...

Jarumin Nollywwood, Mr. Ibu, ya rasu

Jarumin Nollywood, John Okafor, wanda aka fi sani da "Mr Ibu", ya rasu yana da shekaru 62. Emeka Rollas, shugaban kungiyar Actors Guild of Nigeria,...