An bayyana sunan maharin Landan | BBC Hausa

Sudesh Amman
Image caption

Sudesh Amman

Yan sanda sun bayyana sunan mutumin da ya kai hari a kudancin London.

Yan sandan sun harbe maharin bayan da ya dabawa wasu mutane wuka a jiya Lahadi.

Makon da ya gabata ne a ka saki Sudesh Amman, bayan ya shafe shekara daya da rabi daga cikin shekaru uku da aka yanke masa bayan kama shi da laifin ta’addanci.

Tun a lokacin ne a ke sa ido kansa, kafin wannan hari da ya kai da wuka a anguwar Streatham da ke kudancin Landan.

Harin ya jikkata mutane uku kuma daya daga cikinsu na cikin mawuyacin hali.

Firanministan Burtaniya Boris Johnson ya bayyana cewa nan ba da jimawa ba ne gwamnatinsa za ta sauya tsare tsare kan abinda ya shafi matakin sakin wadanda a ka tabbatar yan ta’adda ne.

A cewa mista Johnson akwai bukatar daukar matakin gaggawa kamar kara tsawaita zamansu gidan yari, da kuma kara zuba makudan kudi ga hukumar yan sanda.

Ko a watan Disamba 2019 an kai irin wannan hari a kusa da gadar London wanda ya hallaka wani mai aikin jinkai.

Hakkin mallakar hoto
PA Media

Image caption

An harbe Sudesh Amman bayan ya dabawa mutane uku wuka a wani shago

Rahotanni sun ce Sudesh ya kutsa kai ne wani shago daure da bam din bogi, inda ya rika dabawa mutanen da ke cikin shagon wuka.

To sai dai fitowarsa ke da wuya yan sanda suka bude masa wuta.

A yanzu dai hukumomi sun sanar da cewa kura ta lafa, yayin da su ke cigaba da bincike kan lamarin.

More from this stream

Recomended