Amina Amal Ta Kwanta Jinya Bayan Ta Sha Duka A Hannun Hadiza Gabon

Jaruma Amina Amal ta kwanta rashin lafiya bayan dukan da kawo wuka da fitacciyar Jaruma Hadiza Gabon ta yi ma ta tare da taimakon wasu karti maza.

Majiyar LEADERSHIP A YAU ta tabbatar da cewa, a yanzu haka yarinyar ta na fama da yanayi na rashin lafiya da kuma rudewa sakamakon mumman tashin hankalin da ta fuskanta tun a daren farko da Jaruma Gabon da tawagarta su ka far ma ta a gidanta da ke Kaduna.

Idan za a iya tunawa, Amal ta dora wani hotonta ne a Instagram wanda ke nuna cibiyarta a waje, lamarin da janyo zafafan martani daga masu yin sharhi a kan hoton, ciki har da wasu daga cikin ‘yan fim, kamar ita Gabon da Jaruma Aisha Tsamiya da
Darakta Hassan Giggs da sauransu.

To, amma abin mamaki shi ne Gabon ce kadai wacce Amal ta mayar wa da martani ta hanyar yin shagube kan dabi’a ta madigo, lamarin da ya fusata Gabon din.

Majiya mai tushe ta labarta wa wakilinmu cewa, sau uku ‘yan tawagar sun hada da maza kamar guda biyar ko shida, wadanda wasunsu a motar Hadiza Gabon din su ke yayin da wasu kuma su ke cikin babur din Adaidaita Sahu, cikinsu har da wasu fitattun ‘yan fim guda biyu; daya darakta ne ma.

More News

Zanga-zanga: An jibge Æ´an sanda 4200 a Abuja

Rundunar Æ´an sandan birnin tarayya Abuja ta tura Æ´an sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haÆ™uri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...