Amina Amal Ta Kwanta Jinya Bayan Ta Sha Duka A Hannun Hadiza Gabon

Jaruma Amina Amal ta kwanta rashin lafiya bayan dukan da kawo wuka da fitacciyar Jaruma Hadiza Gabon ta yi ma ta tare da taimakon wasu karti maza.

Majiyar LEADERSHIP A YAU ta tabbatar da cewa, a yanzu haka yarinyar ta na fama da yanayi na rashin lafiya da kuma rudewa sakamakon mumman tashin hankalin da ta fuskanta tun a daren farko da Jaruma Gabon da tawagarta su ka far ma ta a gidanta da ke Kaduna.

Idan za a iya tunawa, Amal ta dora wani hotonta ne a Instagram wanda ke nuna cibiyarta a waje, lamarin da janyo zafafan martani daga masu yin sharhi a kan hoton, ciki har da wasu daga cikin ‘yan fim, kamar ita Gabon da Jaruma Aisha Tsamiya da
Darakta Hassan Giggs da sauransu.

To, amma abin mamaki shi ne Gabon ce kadai wacce Amal ta mayar wa da martani ta hanyar yin shagube kan dabi’a ta madigo, lamarin da ya fusata Gabon din.

Majiya mai tushe ta labarta wa wakilinmu cewa, sau uku ‘yan tawagar sun hada da maza kamar guda biyar ko shida, wadanda wasunsu a motar Hadiza Gabon din su ke yayin da wasu kuma su ke cikin babur din Adaidaita Sahu, cikinsu har da wasu fitattun ‘yan fim guda biyu; daya darakta ne ma.

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...