Ambaliyar ruwa ta yi sanadin mutuwar mayaƙan Boko Haram ‘sama da 100’

Asalin hoton, Nig Army

Gwamman mayaƙa masu iƙirarin jihadi na Ƙungiyar Boko Haram sun mutu a ruwa yayin da suke guduwa daga hari ta sama da ƙasa da sojojin Najeriya ke yi musu a Jihar Borno.

Jami’an tsaron ƙasar sun ce sun kai hari ne a maɓoyar mayaƙan a can cikin dajin Sambisa.

Rahotanni sun ce baya ga farmakin sojojin, akwai ɗaruruwan mayaƙan da suka tsere tare da iyalansu sakamakon ambaliyar ruwa da ta mamaye sansanoninsu.

Mayaƙan sa kai waɗanda ke yaƙar ƴan Boko Haram din sun bayyana cewa sun zaƙulo gawarwaki sama da 100 daga cikin kogi inda suka binne su.

Karin wasu labaran da za ku so ku karanta

Rahotanni sun ce ambaliyar da Kogin Yedzaram ya yi ne ya jawo ambaliyar da ta shafi sansanonin mayaƙan da dama, lamarin da ya ja suka yi hijira.

Dubban mutane ne dai suka mutu, kuma kusan mutum miliyan biyu ne mayaƙan na Boko Haram suka raba da muhallansu.

Sai dai a ƴan kwanakin nan jami’an tsaron ƙasar sun ce ana samun sauƙi sakamakon irn farmakin da suke kai wa mayaƙan.

Haka kuma ana samun wasu daga cikin mayaƙan na Boko Haram da suke tuba suna miƙa wuta.

Kazalika wasu kuma sun bazama inda suke haɗewa da wasu ƙungiyoyi masu iƙirarin jihadin irin su ISWAP da ta fi ƙarfi a arewa maso gabas da kuma ANSARU da ke da ƙarfi a arewa maso takiya da kuma wani fanni na arewa maso yammacin Najeriya.

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...