Ambaliyar Mokwa:Har yanzu ba a gano inda mutane 700 su ke ba

Gwamnatin jihar Niger ta ce mutane sama da 700 ne suka yi batan dabo biyo  bayan ambaliyar ruwa da aka yi a garin Mokwa hedkwatar karamar hukumar Mokwa ta jihar.

Gwamna Umar Bago na jihar shi ne ya bayyana haka lokacin da yake karbar bakuncin, Manjo Hamza Al-Mustapha tsohon dogarin janar Sani Abacha da shi da abokanansa a yayin da suka kai ziyarar ta’aziya da jaje a Minna ranar Talata kan ambaliyar ruwan.

Bago wanda ya samu wakilcin mataimakin gwamnan jihar, Yakubu Garba ya bayyana cewa mutane 207 ne aka tabbatar sun mutu a yayin da wasu 3000 suka rasa muhallinsu.

“Sama da mutane 700 ne  suka bace har kawo yanzu mun gaza gano inda su ke. Ambaliyar tayi barna sosai,” ya ce .

Ya kara da cewa ambaliyar ruwan ta lalata gidaje 400 a yayin da ta ruguza gidaje 283 da shaguna 50.

Bago ya ce gwamnatin jihar na aiki da kungoyin kwararru domin lalubo musabbabin ambaliyar.

Tun da farko Al-Mustapha ya ce sun kawo ziyarar ne domin jajantawa gwamnatin jihar Niger da kuma al’ummar Mokwa biyo bayan mummunan ambaliyar.

More from this stream

Recomended