Al’ummar Jihar Zamfara sun koka game da tashin farashin kayan masarufi

Al’ummar jihar Zamfara sun koka kan hauhawar farashin kayan masarufi.

Wani bincike da waty jaridar Najeriya ta gudanar a wasu manyan kasuwanni a Gusau babban birnin jihar ya nuna cewa farashin kayan masarufi ya karu da sama da kashi 100 a cikin wata guda da ya gabata.

An tattaro cewa baya ga cire tallafin man fetur, barayi sun taimaka ba kadan ba, domin manoma ba za su iya shiga gonakinsu ba, wanda hakan ya haifar da karancin abinci a jihar.

Da yake amsa tambayoyin wakilinmu, wani Suleiman Abubakar, dillalan kayan abinci a babbar kasuwar Gusau, ya ce tashin farashin kayayyakin abinci ya kara tabarbare sakamakon cire tallafin da aka yi a baya-bayan nan.

More from this stream

Recomended