Akwai Ƙarin Wasu Gwamnonin Da Za Su Dawo APC – Ganduje

Shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje, ya bayyana cewa wasu gwamnonin jam’iyyun adawa na shirin sauya sheƙa zuwa jam’iyyar APC kafin zaɓen 2027.

Ganduje ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis a birnin Abuja, yayin da ya karɓi wasu manyan jiga-jigan jam’iyyar NNPP daga jihar Kano ƙarƙashin jagorancin Sanata Kawu Ismaila, wanda ke wakiltar Kano ta Kudu.

A cewar Ganduje, Gwamnan Jihar Delta, Sheriff Oborevwori, da abokin takarar Atiku Abubakar a zaben 2023, Dr. Ifeanyi Okowa, sun sauya sheƙa zuwa jam’iyyar APC tare da wasu ‘yan majalisar tarayya da na jiha, da kuma shugabannin ƙananan hukumomi daga jihar Delta.

Ya ce, “Gwamnan Delta ya koma APC tare da majalisar jiha da ta wakilai gaba ɗaya. Haka kuma dukkan manyan jiga-jigan PDP sun shigo APC, ciki har da tsohon ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa.”


Wasu daga cikin jiga-jigan NNPP da suka sauya sheka sun hada da tsohon Sakataren Gwamnatin Jihar Kano, Hon. Mohd Digol; tsohon kwamishina, Hon. Abbas Abbas; Hon. Sha’aban Ibrahim Lawal; tsohon ɗan takarar gwamna, Hon. Badamasi Ayuba Danbatta; da Hon. Idris Dankuwa, tsohon ɗan Majalisar Wakilai.

Sauran sun hada da Hon. Kabiru Rurmum, Hon. Abdullahi Rogo, Hon. Zubairu Massu, wanda ke cikin Majalisar Dokokin Kano, da kuma Dr. Baffa Bichi.

Wannan sauya sheka na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da fuskantar rikice-rikicen siyasa a jam’iyyar PDP, musamman a lokacin da zaɓen 2027 ke ƙaratowa.

More from this stream

Recomended