Adadin waɗanda suka mutu sakamakon ambaliyar ruwa a Libya ya zarce 6,000

Hukumomin Libya sun ce adadin mutanen da suka mutu sakamakon ambaliyar ruwa da guguwa a kasar ya zarce 6,000.

Sabbin alkaluman da gwamnatin Libiya ta fitar a ranar Larabar sun kara da cewa har yanzu dubban mutane ne suka bace sakamakon wannan mummunan lamari.

A cewar hukumar Majalisar Dinkin Duniya sama da mutane 30,000 ne suka rasa matsuguni sakamakon ambaliyar ruwa.

Wannan na zuwa ne bayan wata mummunar girgizar kasa ta afku a ƙasar Morocco inda sama da mutum 2,000 suka rasa rayukansu, tare da hasarar dukiya.

More News

An samu ambaliyar ruwa a Adamawa

Anguwan Tana, al’ummar karamar hukumar Yola ta Arewa, sun shiga tasgaro a ranar Alhamis sakamakon ambaliya daga kogin Kilange da kogin Faro. Mazaunan garin...

Sojoji sun ceto mutane 6 daga cikin ɗaliban jami’ar Gusau da aka sace

Sojoji sun ceto dalibai mata shida daga cikin daliban Jami'ar Gwamnatin Tarayya dake Gusau da aka bada rahoton yan bindiga sun yi garkuwa da...

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da ɗaliban Jami’ar Tarayya da ke Gusau

An sace wasu daliban jami’ar tarayya ta Gusau da ba a tantance adadinsu ba da sanyin safiyar Juma’a. ‘Yan ta’addan masu yawan gaske sun...

Ƴan sanda sun kama masu safarar makamai wa ƴan bindiga

Jami’an hukumar ‘yan sanda reshen Karasuwa a jihar Yobe sun cafke wasu mutane biyu da ake zargi da kai wa ‘yan bindiga makamai da...