Gwamnatin Fiilato ta ce bata yi wa ‘yan Chinar nan uku da aka killace gwajin cutar coronavirus ba domin gano ko suna dauke da cutar ko kuma ba su da ita.
Kwamishinan lafiya na jihar Dakta Nimkong Ndam ne ya shaida wa BBC hakan inda ya ce ko da jami’ansu suka je wurin ‘yan Chinar da aka killace, sun yi musu tambayoyi ne kawai da kuma duba takardunsu.
Ya bayyana cewa sun gano cewa an yi wa ‘yan Chinar gwaji a Addis Ababa, haka kuma da suka sauka a Abuja ma an yi musu gwaji, wannan dalili ne ya sa suka gamsu da cewa babu wasu alamun cutar tattare da su.
Ya ce ”Mun duba cewa an yi musu gwaji, sun zo a kan ka’ida, suna da takardun tafiya”.
Sai dai ya bayyana cewa za su ci gaba da zama killace sai zuwa 11 ga watan Maris kafin su fara walwala cikin jama’a kamar kowa.
Mista Ndam ya kuma kara bayar da shawara kan duk wanda ya yi tafiya zuwa wata kasa da aka samu bullar cutar coronavirus, mutum ya killace kansa da kansa zuwa a kalla mako biyu kafin ya fara shiga cikin mutane.
A ranar Asabar ne dai ma’aikatar lafiya a jihar Filato da ke arewa maso tsakiyar Najeriya ta tabbatar da killace wasu ‘yan kasar China uku saboda fargabar coronavirus.
Lamarin ya faru ne bayan wasu ‘yan kasar Chinar uku da ke aiki a wani wurin hakar ma’adanai a garin Wase sun dawo daga tafiya.
Wannan ne ya sa da isarsu kamfanin, sai ‘yan uwansu ‘yan China wadanda ba su yi tafiya ba suka hana su shiga kamfanin sakamakon tsoron da suke yi ko kuma fargabar kada a ce sun dauko musu cutar coronavirus sun kawo musu.
Wannan dalilin ne ya sa ma’aikatar lafiya tare da hadin gwiwar hukumar da ke kula da shige da fice da kuma ‘yan sanda suka tura tawaga zuwa garin Wase domin likitoci su yi musu gwajin cutar ta coronavirus.